Switch to Hausa

Switch Now
Latest

Gwamnatin jahar Bauchi ta karyata labarin dake dangantata da mara baya wa shirin shiga zanga zanga na kasa baki daya

Gwamnatin jahar Bauchi ta karyata shirye shiryen shiga cikin zanga zanga na kasa baki daya da za’a fara a ranar daya zuwa ranar Sha biyar ga watan agosta.

Sakataren gwamnatin jahar Bauchi Barista Ibrahim Kashim ne ya fada hakan a lokacin wani taron manema labarai da yayi a gidan gwamnatin jahar Bauchi.

Barista Ibrahim Kashim ya jaddada cewar gwamnatin jahar Bauchi bata da wata masaniya, kuma bata maraba da duk wani nau’i na zanga zanga a jahar.

Ya kuma gargadi masu so suyi zanga zangar da suyi tsam da ransu kafin yin wani yunkuri na shirya duk wani taro a Bauchi,yana mai jaddada cewar, gwamnatin jahar bazata lamunci duk wani yunkuri na karya doka da oda ba.

Taron manema labaran ya zone a daidai wani lokaci ake watsa wasu ya madidi cewar gwamnatin jahar Bauchi ta amince zata rufe cibiyoyin Kula da kiwan lafiya a ranar da aka tsara za’a gudanar da zanga zangar.

Ibrahim Kashim ya karyata wannan ikirari,yana fadin cewar gwamnatin jahar Bauchi bata da wata masaniya ko shiga cikin wannan matsaya.

A cewar sa an kaddamar da bincike domin gano jami’in da ya watsa wadannan bayanai dan daukar mataki,ya Kuma bada tabbacin cewar dukkan cibiyoyin Kula da lafiya a matakin farko da sauran cibiyoyi na gwamnatin jahar Bauchi zasu cigaba da zama a bude,domin kuwa a cewar sa gwamnat ta himmatu domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button